Posts

AM I ALIVE?

I spotted a small bird, walking wearily. Concerned, I asked, ‘What happened, dear friend? Are you sick?’ The bird forced a feeble smile, one that seemed on the brink of death, and replied, ‘I am non-living things.’ I chuckled, but before I could speak, it continued, ‘Sometimes, I feel like a dying bird. I don’t know if I’m right or wrong. Life itself is a maze of confusion. If we’re here on earth to relish our existence, then I believe I am not alive. However, if we’re here to endure, suffer, and suffer some more, then I am alive. We only have one life, and it’s brimming with suffering. But no matter how dire the situation, I don’t want to die, for true death is even more dreadful than living.’ Naseeb Auwal 

EYE OPENER... (SIWES)

Image
Alhamdulillah! I was not just introduced to the Center for Bioresources; I was introduced to a wonderland of science. It is a place where waste is utilized to produce valuable products, where the seemingly impossible becomes possible. This place is teeming with opportunities for those who are ready to embrace them. In this world of science, good researchers and hardworking scientists work diligently to harness the potential of bioresources, finding creative ways to transform waste into valuable materials. Through their efforts, they contribute to sustainable practices, resource conservation, and the development of eco-friendly alternatives. Being introduced into this realm of science is full of responsibilities, dedication of time and energy as well as money (transportation, especially for students like me), curiosity, and a willingness to push the boundaries of what is known. It offers the chance to make meaningful contributions and be part of groundbreaking advancements t

HAKA MISALINKI YAKE!

HAKA MISALINKI YAKE!!! Wata ɗaliba ce a wata makaranta, bayan sun kammala karatun zango sai aka tsara musu jarrabawa, amma abin mamaki sai ta ƙi rubuta komai a takardarta duk da tana ganin ƴan uwanta sun duƙufa suna ta rubutu... Bayan an karɓe takardunsu duka sai ɗalibai suke tattaunawa akan wannan jarrabawa, sai wannan ɗaliba tace ai ita babu abin da ta rubuta alhalin ta sani kuma tana sane, "AISHI ILMI BA A TAKARDA YAKE BA, A ƘWAƘWALWA YAKE..." a cewar wannan ɗaliba. Sauran ɗalibai suka ɗauka da wasa take, sai da jarrabawa ta fito sai suka ganta tana ta kuka. Wata ƙawarta ta zo kanta ta tsaya tace "KINGA ABIN DA MUKE JIYE MIKI KO? RUBUTUN DA ZA KAI A TAKARDAR JARRABAWA SHI NE YAKE NUNA CEWA TABBAS KAYI KARATU, KUMA AKWAI KARATUN A KWAKWALWARKA." Yar'uwa wannan shi ne misalin matan da suke shigar banza kuma suke fakewa da cewa IMANI A ZUCI YA KE. Wannan shi ne misalin matan da suke ƙin yin biyayya ga Allah a aikace suna da'awar ai imani a zuci ya ke. Wannan

JAN HANKALI GA ƊALIBAN KIMIYYA

Sai yanzu na gane... Na riski maganganun malamai da yawa da suke cewa "Qur'anin ba littafin kimiyya ba ne, littafin shari'a ne. Sai dai ana samun ilmin kimiyya a cikinsa a matsayin mu'ujiza..." A lokutan baya sai in rasa menene hikimar yin wannan togaciya cewa Qur'ani ba littafin kimiyya ba ne. Yanzu kam alhamdulillah na gano wasu daga cikin dalilan da yasa malamai suke wannan maganar. Ga kaɗan daga ciki. ★ Dalilin saukar da Qur'ani shi ne shari'a, don haka duk wani abu da za a samu a cikinsa koma bayan shari'a ne. Don haka, idan aka ɗauki ayar Qur'ani mizanin da za a fassarata da shi, shi ne mizanin mutanen da Qur'anin ya sauka a cikinsu (Sahabbai). Su kuwa Sahabbai ana samun bayanai akansu ne a cikin littafan sunnah ingantattu. To ashe idan muka samu aya magabata sun fassarata da wata ma'ana, to ɗaukar abin da suka fassarata da shi, shi ne dai-dai. Maganar wasunsu daga ɓangaren malamai ko masana kimiyya tana iya biyo baya mutuƙar bata

MUTUM DA HANKALI

Image
Mutane da Hankali 01 Da sunan Allah mai rahama mai jin ƙai. Tsira da amincin Allah su tabbata ga Shugaba, Ja gaba, tare Ahalinsa da Sahabbansa.  Hankali shi ne mafi girman abin da Allah ya bawa ɗan Adam, ba wai don bai bawa sauran halittu shi ba, sai don yanda ɗan Adam yake amfani da hankalin na sa ya sha bambam da yanda sauran halittu suke amfani da na su hankalin. Hakan kuma ya samo asali ne saboda shi tunanin ɗan Adam yana samun jagoranci ne daga shari'a wadda Allah ya aiko manzanni da ita, don haka sai ɗan Adam ya zamana yayi fintinkau a ɓangaren kowace ɗabi'a mutuƙar.  Wani zai ce ai tun kafin a saukar da Shari'a mutum ya ke da hankali, sai mu ce, Allah da ya halicci Annabi Adam, ya halicceshi ne akan fiɗira, kuma haka aka ɗorawa Annabi Adam nauyin ɗora ƴaƴansa akan wannan tafarki wanda aka ɗorashi a kai.  Allah Mai Girma da Ɗaukaka ya na cewa: كَانَ النَّاسُ أُمَّةً وَاحِدَةً فَبَعَثَ اللَّهُ النَّبِيِّينَ مُبَشِّرِينَ وَمُنذِرِينَ وَأَنزَلَ مَعَهُمُ الْكِ

ƘARYA

Image
ƘARYA. DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN ƘAI, TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA GA ANNABIN RAHAMA SHUGABA JA GABA DA AHALINSA TARE DA SAHABBANSA DA WAYANDA SUKA BIYO BAYANSU DA KYAUTATAWA. NA SHAIDA BABU ABIN BAUTAWA DA GASKIYA SAI ALLAH KUMA ANNABI MUHAMMAD BAWANSA MANZONSA NE.  HAKIKA MAFI GASKIYAR ZANCE SHINE LITTAFIN ALLAH, KUMA MAFI ALHERIN SHIRIYA ITACE SHIRIYAR ANNABI MUHAMMAD (S.A.W), MAFI SHARRIN AL'AMURA KUWA SUNE WAYANDA AKA FARAR, KUMA DUKKANIN FARARREN ABU BIDI'A NE, KUMA DUKKANIN BIDI'A ƁATA CE. BAYAN HAKA, WANNAN WANI TAƘAITACCEN RUBUTU NE DA NAKE SO IN BIJIROWA YAN UWA SHI DON TUNATARWA DA KUMA FAƊAKARWA AKAN WANI MUHIMMIN ABU MAI GIRMA WANDA SABO DA SHI YA SANYA DA YAWANMU MUN DAINA GANIN GIRMANSA. BA WANI ABU BANE WANNAN FACE ƘARYA.  INA ROƘON ALLAH DA YA SANYA WANNAN AIKI YA ZAMO DON SHI AKAYI, YA KUMA KARƁI AIKIN, HAƘIƘA SHI MAI IKO NE MAI KUMA KARAMCHI NE. ƘARYA Ƙarya dai sananniyar aba ce, domin kuwa koda yaushe tana kaikawo a cikin mutane,

LALLAI AKWAI TAMBAYA DANGANE DA NI'IMOMIN RAYUWA

“Sa'annan kuma haƙiƙa lallai sai an tambayeku game da ni'imomi.”  Duk wata ni'ima ta shiga cikin wannan, don haka idan Allah ya yiwa bawa wata ni'ima to tabbas ya shirya amsa tambayoyi ranar alƙiyama akan wannan ni'imar. Cikin hadisi ingantacce riwayar muslim, Annabi Muhammad (S.A.W) da manyan sahabbansa da kuma mafi kusancin abokanansa (Abubakar da Umar) (R.A) yunwa ta fito da su, a ƙarshe suka samu abinci a gidan ɗaya daga cikin sahabbai mawadata, suka ci suka ƙoshi kuma Annabi ya basu tabbacin cewa sai an tambayesu dangane da wannan ni'imar. Idan har abincin da ba kai ka nemo da guminka ba za'a tambayeka to ni'imomin da akai maka na lafiya da ƙwarewa a wani fanni na rayuwa sune mafi aula da'a tambaya. Idan kanada ƙarfin tunani da hangen nesa to tabbas za'a tambaye ka akan wannan ni'imar. Idan kana da fasahar tsara rubutu to tabbas za'a tambaye ka akan hakan. Idan kana da balagar magana, ka iya yin magana wadda za'a fahimta kuma ka