Posts

Showing posts from December, 2024

SHARHIN HADISI NA 19

Daga Ibn Abbas Allah ya yarda da su yace "Wata rana na kasance a bayan Annabin rahama, sai yace da ni "Ya kai yaro, ka kiyaye (dokokin) Allah, zai kiyaye ka. Ka kiyaye (dokokin) Allah, za ka same shi a gabanka. Idan za kai roƙo, ka roƙi Allah. Idan za ka nemi taimako, ka nemi taimakon Allah. Kuma ka sani, lallai da al'umma za su taru don su amfanar da kai da wani abu, ba za su amfanar da kai da komai ba, sai da abin da Allah ya rubuta a gareka. Kuma haka nan da za su taru don su cutar da kai da wani abu, ba za su iya cutar da kai ba, sai da abin da Allah ya rubuta a gareka. An ɗage alƙaluma, kuma takardun sun bushe... Wannan ruwayar Imam Tirmidhi ce, kuma sanadin ingantacce ne. Wannan hadisi ya tattare bayanai da fa'idoji da yawa wanda kowace fa'ida a ciki abar ayi rubutu mai zaman kansa ne akanta, amma inshaa Allah zamu taƙaita a rubuce rubuce masu zuwa. A cikin wannan hadisi a jimlace za mu gane sauƙin kan Manzon Rahama, domin dukkanin wayannan muhimman magangan...