Posts

Showing posts from September, 2026

BAMBANCIN BIN ALLAH DA BIN ƘUNGIYA

Image
BAMBANCI... Tambayi kanka : Shin kana bin abin da Allah da Manzonsa ﷺ suka umarta ne, ko kana neman hujja ne kawai domin kare abin da ka riga ka yarda da shi? BIN ALLAH DA MANZONSA ﷺ Musulmi na gaskiya yana ɗaukar Qur’ani da ingantacciyar Sunnah a matsayin ma’aunin gaskiya. Duk lokacin da ya san hukuncin Allah da Manzonsa ﷺ a kan wani abu, abin da ake buƙata daga gare shi shi ne sallamawa da biyayya, ba neman wata hanya ta fifita son rai ko al’ada ko ra’ayin wani a kan dalilin  ba. Allah Ya ce: يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا أَطِيعُوا اللَّهَ وَأَطِيعُوا الرَّسُولَ وَأُولِي الْأَمْرِ مِنكُمْ ۖ فَإِن تَنَازَعْتُمْ فِي شَيْءٍ فَرُدُّوهُ إِلَى اللَّهِ وَالرَّسُولِ “Ya ku waɗanda suka yi imani! Ku yi biyayya ga Allah, kuma ku yi biyayya ga Manzo, da ma'abota al'amari (ilmi ko shugabanchi) daga cikinku. Idan kuka yi saɓani a kan wani abu, ku mayar da shi zuwa ga Allah da Manzo...” [An-Nisā’ 4:59]. Ka lura da abin da Allah Ya koyar: idan aka samu saɓani, a mayar da al’amari zuwa ga A...